Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau ya sanar da kudurinsa na tsayawa takarar shugabancin kasar nan a karkashin jam’iyyar PDP a...
Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Malam Ibrahim
Shekarau ya sanar da kudurinsa na tsayawa
takarar shugabancin kasar nan a karkashin
jam’iyyar PDP a zaben 2019.
Shekarau tsohon gwamnan kano kuma tsohon
Ministan Ilimi ne ya yi wannan jawabin ne a wata takarda da aike
wa Aminiya, inda ya ce zai tsaya ne domin ya
amsa kiran mutane. “Kamar yadda kuka sani ne,
tun bayan zaben 2015, mutane da kungiyoyi
dabam daban suna kiraye-kiraye da in tsaya
takarar shugaban kasa a zaben 2019. “Na yi imanin cewa mutanen suna kira na ne saboda
sun yarda ni kuma sun amince da ni bisa da
nasarar da aka samu a lokacin da nake
Gwamnan Jihar Kano a tsakanin shekarar 2003
zuwa 2011, da kuma lokacin da nake Ministan
Ilimi a tsakanin watan Yuli na shekarar 2014 zuwa watan Mayu na shekarar 2015. “Saboda
wannan kiraye-kiraye da ake min da kuma
girman aikin da suke kira na yi.
Na yi tuntuba mai fadi a duk bangarorin kasar
nan, inda suke duba sannan kuma suka bani
shawarar da ta dace. “Ina mai farin cikin cewa, bayan na yi wannan tuntuba, na kara fahimtar
cewa shiga siyasa da nufin amfanar da mutane ya
wuce maganar jam’iyyar da kuma maganar lashe
zabe kawai. “Don haka na amince zan amsa kiran
mutane, sannan kuma nan ba da dadewa ba
kamar yadda dokokin jam’iyyata ta PDP ta kindaya, zan tsaya takarar shugabancin kasar
nan a zaben 2019.” Inji Shekarau.
.
Source by @Aumarblog
COMMENTS